“Ba za mu auna nasarar da muka samu ta fuskar yaƙe-yaƙen da muka yi nasara kadai ba, ko yake-yaken da muka dakatar ba – za mu hada har da yakin da ba mu shiga ba.”
Ambasada Wood ya ce: "Babu wata gardama cewa Iran, a fili take keta takunkumin makamai a cikin kudiri na 1701, tana ba Hezbollah mafi yawan makaman roka, makamai masu linzami da jirage mara matuka da ake harbawa Isra'ila."
Yanzu akwai rahotannin da ke cewa kawancen soji tsakanin Iran da Rasha na karuwa, kamar yadda babban mataimakin kakakin ma'aikatar harkokin wajen Amurka Vedant Patel ya bayyana a wani taron manema labarai na baya-bayan nan
Amurka na kira ga Janar Abdel Fattah al-Burhan da Hemedti da su halarci tattaunawar tsagaita bude wuta a Switzerland a ranar 14 ga watan Agusta.
Babu shakka, kwata-kwata babu, Hezbollah ce ke da alhakin wannan harin, wanda ya yi amfani da makamin Iran, kuma an harba shi daga wani yanki na Lebanon da Hezbollah ke iko da shi."
“Abin mamaki ne yadda al’ummar da ke cikin tsananin talauci a duniya take samun damar maraba da mutane da yawa da suke da bukata."
Amurka ta kuduri aniyar yin aiki kafada da kafada da gwamnati da jama'ar Kenya yayin da suke kokarin magance kalubalen tattalin arzikinsu, tare da tabbatar da kare hakkin bil'adama a Kenya da ma duniya baki daya.
'Yancin walwalar addini na ci gaba da fuskantar barazana ga miliyoyin mutane a sassan duniya, in ji Sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken
"Saboda haka, a bayyane yake shirye-shiryen Isra'ila na biyan bukatun mutanen da suka rasa matsugunansu ba su wadatar ba." in ji Ambassador Wood.
“Waɗannan mutane biyu ne da ake zargi da hannu a kisan kiyashin da aka yi a Rwanda a shekara ta 1994. Don haka, har yanzu ana bayar da tukwici ga bayanan da za su kai ga kama su.”
“Muna kira ga Vietnam da ta mutunta ‘yancin fadin albarkacin baki, tarayya, da addini ko imani." Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Amurka Matthew Miller ya ce.
Load more